Post Top Ad

Post Top Ad

Tuesday, October 2, 2018

POLITICS: Mataimakiyar gwamnan Legas ta juya masa baya, tana goyon bayan abokin takarar sa

Hakan ya fito yayin da jam'iyar APC reshin jihar take gudanar da zabe na tantance wanda zai jagoranci jam'iyar a zaben gwamna na 2019.


Mataimakiyar gwamnan jihar Legas, Idiat Adebule, ta nuna goyon bayan ta da abokin takarar mai gidan ta na zaben fitar da gwanin jam'iyar APC.

Hakan ya fito yayin da jam'iyar APC reshin jihar take gudanar da zabe na tantance wanda zai jagoranci jam'iyar a zaben gwamna na 2019.


Sakamako dake fitowa daga wasu mazabu na jihar na nuna cewa gwamna Akinwunmi Ambode na fuskantar zagon kasa inda babba abokin takarar sa kuma dan takarar da mafi yawancin jiga-jigan jam'iyar ke goyon baya, Babajide Sanwo-Olu,yayi zarra.

Hajiya Idiat ta bayyana ra'ayin ta game da wanda take goyon baya yayin da take kada kuri'a a mazabar ta dake nan Ward A na karamar hukumar Iba.

Tace "Jam'iya ta fitar da dan takara kuma nima shi zan mara ma baya".


Rahotanni sun bayyana cewa wasu masu yi ma mataimakiyar gwamnan hidima da  magoya bayan ta sun garzaya wajen kada kuri'a da fosta na mara ma Sanwo-Olu baya.

No comments:

Post a Comment